--
Yadda kowa yabi ya tsaneni saboda na auri bakar fata – Baturiya ta bayyana labarinta mai ban tausayi

Yadda kowa yabi ya tsaneni saboda na auri bakar fata – Baturiya ta bayyana labarinta mai ban tausayi



Wata Baturiya ‘yar kasar Bulgaria, ta nuna damuwarta akan wariyar launin fata, da kuma yadda ake cin zarafin mutane saboda kalar fatarsu.

Ta ce a kauyen da ta taso na Shumen, dake kasar ta Bulgaria, mutanen kauyen suna da wata matsala da babu dama su ga wani ya auri mutumin da ba kalar shi ba sai su fara maganganu marasa dadi.

Matar mai suna Elina ta ce dole ya sanya suka koma cikin birni da zama, suka fara sabuwar rayuwa, amma duk da haka rayuwar ba sauki.

Ta ce sun kasa samun gidan da za su kama haya, saboda yanayin kalar fatar mijinta, ta ce a lokacin ne ta san abinda ake kira da wariyar launin fata.

Elina ta ce ita tana daukar mutum da muhimmanci ne ta hanyar la’akari da dabi’u, soyayya, kirki da kuma mutuntaka. Ta kara da cewa tana fatan lokaci zai zo da mutane za su daina wannan bakar al’adar ta nuna wariya ga wasu mutane daban.

Wannan dai na zuwa ne yayin da ake ta faman zanga-zanga manyan kasashe na duniya akan nuna wariyar launin fata da ake yi a kasashen Turawa musamman ma ga bakar fata.

Zanga-zangar ta samo asali ne bayan kashe wani mutumi mai suna George Floyd da ‘yan sandan kasar Amurka suka yi babu gaira babu dalili, saboda kawai Allah yayi shi bakar fata.




KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657


0 Response to "Yadda kowa yabi ya tsaneni saboda na auri bakar fata – Baturiya ta bayyana labarinta mai ban tausayi"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?