--
Tsawa ta fada kan ofishin FRSC a jihar Kudu ta kashe jami'ai 3 ta buga fiye da 12 a kasa

Tsawa ta fada kan ofishin FRSC a jihar Kudu ta kashe jami'ai 3 ta buga fiye da 12 a kasa



ROHOTON: ISYAKU.COM

Tsawa ta fada wa ofishin jami'an FRSC na Itele-Ijebu da ke kan hanyar Ijebu-Ode-Ore ta kuma kashe mutum uku ta watsar da sauran mutane a kasa ranar Laraba 17 ga watan Yuni da sanyin safiya.

Lamarin ya faru da misalin karfe 10 na aafe a tsohon Toll gate na tagwayen hanya, wanda haka ya jefa rundunar jamai'an FRSC na jihar Ogun cikin alhini.

Mun samo cewa jami'an suna kokarin gudanar da paretin safe da aka saba a harabar ofishinsu, sai tsawa ta fada masu. Nan take mutum 3 suka mutu , saura kuma suka fadi sakamakon radadin wutan lantarki da tsawar ta watsa masu wanda ya shafi fiye da mutum 12.

Jami'in wayar da kan al'umma da fadakarwa na rundunar FRSCna jihar Ogun Florence Okpe ya tabbatar da faruwar lamarin, sai dai ya ki ya ce uffan ko karin bayani.


KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Tsawa ta fada kan ofishin FRSC a jihar Kudu ta kashe jami'ai 3 ta buga fiye da 12 a kasa"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?