--
Da dumi duminsa: Gwamnatin tarayya ta rage kudin aure a Najeriya

Da dumi duminsa: Gwamnatin tarayya ta rage kudin aure a Najeriya



ROHOTON  PRESSLIVES: https://presslives.com/
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta rage kudin gudanar da aure a Najeriya. Sabon kudin da ta sanya zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Yuli.

Sabon kudin ya zo karkashin dokar aure ta CAP M6 LFN 2004, a cewar sanarwar da babban sakatare kuma mai rijistar aure a Najeriya, Georgina Ehuriah.

Wata sanarwa daga daraktan yada labarai na ma’aikatar cikin gida ta Najeriya, Mohammed Manga, ta bayyana cewa hakan wani garambawul ne da gwamnati za tayi a fannin auren bayan samun shawarwari daga masu ruwa da tsaki a kwanan nan.

Lasisin yin aure a wuraren bauta an rage shi daga N30,000 na tsawon shekara biyu zuwa N6,000 a kowacce shekara.

Sabunta lasisin auren a wajen bauta, an amince a dinga biyan N5,000 a kowacce na tsawon shekara uku. Yayin da a da yake N30,000 kowacce shekara.

Hakanan an rage kudin daurin aure daga N21,000 zuwa N15,000, inda aka rage kudin lasisi na musamman daga N35,000 zuwa N25,000.

A kwanakin baya mun kawo muku rahoton fitacciyar jarumar fina-finan kudancin Najeriya na Nollywood, wacce ta bukaci a daina biyan kudin aure baki daya.

Toni Tones dai ta ce mata ba kadarori bane da za a ce duk lokacin da za ayi aure sai an biya musu sadaki ba. Ga dai cikakken labarin: Kamata yayi a haramta bayar da sadaki ga mata a lokacin aure – Toni Tones


KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
 LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Da dumi duminsa: Gwamnatin tarayya ta rage kudin aure a Najeriya"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?