--
Tsohon shugaban kasa Abdulsalami Abubakar ya tofa albarkacin bakinsa kan tsige sarki Sanusi da aka yi

Tsohon shugaban kasa Abdulsalami Abubakar ya tofa albarkacin bakinsa kan tsige sarki Sanusi da aka yi

- Shugaban wani kwamitin yin sulhun a tsakanin tsohon Sarki Muhammadu Sanusi da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jahar Kano, Abdulsalam Abubakar ya ce sun yi iya kokarin bakinsu domin ganin sun kawo sasanci a tsakanin shugabannin biyu - Abdulsalam ya nuna alhini kan lamarin tsige Sarki Sanusi da gwamnatin Kano ta yi 

- Ya ce ba shi da masaniya ko shugaba Buhari ya sa baki ko a'a Tsohon shugaban kasa, Abdulsalami Abubakar, wanda shine shugaban wani kwamitin yin sulhun a tsakanin tsohon Sarki Muhammadu Sanusi da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jahar Kano, 

da samar da zaman lafiya a Najeriya, ya bayyana cewa sun yi iya kokarin bakinsu domin ganin sun kawo sasanci a tsakanin shugabannin biyu, amma abun ya ci tura. A wata hira da ya yi da muryar Amurka, Abdulsalami, ya ce duk da yake sun zauna a lokuta mabanbanta da gwamnan jahar Kano da kuma tsohon sarki Sarki Sanusi na biyu, kafin suka yi wani zaman tare da su a lokaci daya, hakarsu bata cimma ruwa ba na neman a sasanta su, har abun ya kai ga tsige Sarkin, kasancewa gwamna ne mai wuka kuma mai nama. 

Tsohon shugaban kasa Abdulsalami Abubakar ya tofa albarkacin bakinsa kan tsige sarki Sanusi da aka yi Source: Twitter Game da batun sa bakin Shugaban kasa Muhammadu Buhari wajen sulhunta rashin jituwar, tsohon Shugaban kasar ya ce ba shi da masaniya ko shugaba Buhari ya sa baki ko a'a. Kuma cewa idan har ya sa baki da mamaki a kai inda ake yanzu. 

Ya kuma yi addu’ a kan Allah ya zaunar da jahar Kano lafiya sannan ya kuma kawar da fitina da kawo sauki, cewa duk abunda Allah ya kaddara babu mai iya canja shi. A wani lamarin kuma, mun ji ceewa shugaban kungiyar Arewa Youth Organizations ta Matasan Arewacin Najeriya, Murtala Abubakar, ya yi magana game da tsige Sarki da gwamnati ta yi a kasar Kano. Mista Murtala Abubakar ya bayyana cewa akwai laifin shugaba Muhammadu Buhari wajen wannan mataki da gwamnatin jihar Kano ta dauka na tunbuke Sarkin Birni.

LATSA NAN👇👇👇 DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI TA WHATSAPP https://chat.whatsapp.com/BztTOlXx6c183yYthtZq1Y

KU BIYOMU TA FACEBOOK FAGE DINMU KUYI LIKE DOMIN SAMUN LABARI 




0 Response to "Tsohon shugaban kasa Abdulsalami Abubakar ya tofa albarkacin bakinsa kan tsige sarki Sanusi da aka yi "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?