--
Tsige Sanusi: 'Ba ni na kar zomon ba'; Fatima Ganduje ta yi wa masu sukarta martani

Tsige Sanusi: 'Ba ni na kar zomon ba'; Fatima Ganduje ta yi wa masu sukarta martani


- Diyar gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, Fatima Ajimobi, ta bukaci mutane da su daina saka ta cikin lamarin da ya faru a jiya Litinin - Hakan ya biyo bayan zagi da cin zarafi da take fuskanta daga jama'a a kafafen sada zumuntar zamani 


- Fatima dai daya daga cikin 'yayan gwamnan jihar Kano din ce wacce ke auren dan tsohon gwamnan jihar Oyo, Abiola Ajimobi Diyar gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, Fatima Ajimobi ta bukaci mutane da su daina saka ta cikin lamarin da ya faru a jiya Litinin na tsige sarki Sanusi daga karagar mulkin jihar Kano. Hakan ya biyo bayan zagi da cin zarafi da take fuskanta daga jama'a a kafafen sada zumuntar zamani. Ta bukaci mutane da su daina kiran sunanta tare da jawo hankalinta a duk lokacin da zasu yi maganar lamarin.

Tsige Sanusi: 'Ba ni na kar zomon ba'; Fatima Ganduje ta yi wa masu sukarta martani Source: Facebook


Fatima dai daya daga ckin 'yayan gwamnan jihar Kano din ce wacce ke auren dan tsohon gwamnan jihar Oyo, Abiola Ajimobi. Wasu daga cikin ma'abota amfani da kafar sada zumuntar zamani sun dinga zagin gwamna Ganduje tare da kiran sunan Fatima Ajimobi a wallafar ta yadda hankalinta zai kai. A take kuwa ta wallafa cewa a daina kiran sunanta don ba ita ta kashe zomon ba.LATSA NAN👇👇👇 DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI TA WHATSAPP https://chat.whatsapp.com/BztTOlXx6c183yYthtZq1Y

KU BIYOMU TA FACEBOOK FAGE DINMU KUYI LIKE DOMIN SAMUN LABARI 




0 Response to "Tsige Sanusi: 'Ba ni na kar zomon ba'; Fatima Ganduje ta yi wa masu sukarta martani "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?