--
Yadda barayin mutane suka sace wannan yarinyar Sukayi mata Gunduwa Gunduwa Bayan sun karbi kudin Fansa A Kano

Yadda barayin mutane suka sace wannan yarinyar Sukayi mata Gunduwa Gunduwa Bayan sun karbi kudin Fansa A Kano


Duk da karbar wani bangare na Naira miliyan 6 da masu garkuwa da mutane suka nema, wadanda suka sace wata yarinya ‘yar Jihar Kano mai suna Hanifa Abubakar ‘yar shekara 5, sun kashe ta.

Kawun Yarinyar, Mai suna Suraj Suleiman, ya tabbatar da kasheta tare da tsintar gawarta a wata makaranta mai zaman kanta da ke unguwar Tudunwada a Kano.

A cewarsa, wanda ya sace ta ya fara kai ta wurin matarsa, amma matar ta ki ci gaba da rike ta.


“Mai garkuwa da mutanen ya fara kai Hanifa wurin matarsa, amma matar ta ki rike ta. Daga nan sai ya kai ta Tudunwada inda yake gudanar da wani makaranta mai zaman kansa, sannan ya kasheta ta hanyar bata shayi da gubar bera,” inji kawunta.


"Bayan an saka mata guba ta mutu, sai masu garkuwa da mutanen suka yanka gawarta gunduwa-gunduwa suka binne a cikin makarantar."


DAILY NIGERIAN ta tattaro cewa an cafke masu garkuwa da mutanen, a kusa da titin Zaria a Kano a daren jiya a lokacin da suke kokarin karbar kaso na biyu na kudin fansa.


Masu garkuwa da mutane sun yi garkuwa da yarinyar mai shekaru 5 a ranar 4 ga Disamba, 2021, wadanda suka zo akan babur din Adaidaita Sahu inda suka yaudare ta ta shiga cikin farin ciki.


Lamarin ya faru ne da karfe 5 na yamma lokacin da ita da sauran yaran unguwar suke dawowa daga makarantar islamiyya.

0 Response to "Yadda barayin mutane suka sace wannan yarinyar Sukayi mata Gunduwa Gunduwa Bayan sun karbi kudin Fansa A Kano"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?