--
Yanzu yanzu: Buhari ya bada umurnin bude iyakokin kasa guda huɗu

Yanzu yanzu: Buhari ya bada umurnin bude iyakokin kasa guda huɗu

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce a bude iyakoki guda hudu - Shugaban kasar kuma ya ce a bude sauran iyakokin kasar zuwa karshen shekara Shugaba Muhammadu Buhari ya bada umurnin bude iyakokin kasa guda hudu ba tare da bata lokaci ba kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito. 


A umurnin da ya bada a ranar Laraba, shugaban kasar ya kuma bada umurnin bude sauran iyakokin kasar zuwa ranar 31 ga watan Disambar 2020.



Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya bayar da umarnin bude wasu iyakokin kan tudu guda hudu 


Ministar Kudi ce ta sanar da hakan yayin tattaunawa da manema labarai bayan kammala taron FEC:



Labari da dumi-duminsa da Jaridar Legit.ng Hausa ta samu daga shafin gidan talabijin na Channels ya bayyana cewa shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya bayar da umarnin bude iyakokin kan tudu guda hudu. 


A cikin takaitaccen kanun labarai da Channels ta wallafa, ta bayyana cewa umarnin bude iyakokin zai fara aiki ne daga ranar 31 ga watan Disamba, 2020.


Iyakokin guda hudu da za'a bude sune kamar haka: Illela a Jihar Sokoto, Maigatari a jihar Jigawa, dukkansu a arewacin Nigeria. Sai kuma iyakar Seme da ke Jihar Legas, yankin kudu maso yamma, da iyakar Mfun da ke yankin kudu maso kudu. 


Daily Nigerian ta rawaito cewa ministar kudi, Zainab Ahmed, ce ta sanar da hakan ranar Laraba yayin ganawarta da manema labarai jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa ta tarayya (FEC). 


Sanarwar bude iyakokin na zuwa ne a daidai lokacin da kungiyar NSMC ta kwatanta rashin tsaron Najeriya da rashin tsaron iyakoki, inda ta bayyana cewa hakan ne dalilin da yasa aka gaza cin nasara akan 'yaki da 'yan bindiga da Boko Haram. 


Ta ce matsawar gwamnatin tarayya tana son cin nasara a kan rashin tsaro ta wuraren tafkin Chadi, wajibi ne a kula kwarai, kamar yadda Daily Trust ta wallafa. 


Wadannan kadan ne daga cikin hanyoyin da za a tsare 'yan Najeriya daga cutarwar 'yan bindiga, kamar yadda mambobin kwamitin suka tattauna don samar da tsaro a kasar nan. 


SOURCE: LEGIT


Mtn Data Bonanza By Bz Global Services 🌐

1GB @N350 

2GB @N700

3GB @N1,050

4GB @N1,400

5GB @N1,750

Validity For 30Days

Hanyar Biya Bank Transfer Domin Siya Yanzu Kiramu Ta Number Waya 08133888333 Koka Aiko Sako Ta Whatsapp: 09066633320


LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A WHATSAPP:

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A TELEGRAM:


KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app75765

0 Response to "Yanzu yanzu: Buhari ya bada umurnin bude iyakokin kasa guda huɗu "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?