--
Zukekiyar budurwa ta wallafa hotonta tana neman saurayi, ta ce kada talakan da ya kawo kansa

Zukekiyar budurwa ta wallafa hotonta tana neman saurayi, ta ce kada talakan da ya kawo kansa


Wata budurwa mai suna Adanna ta wallafa kyakyawan hotonta a Twitter tana neman saurayi - Sai dai , ta bayyana cewa gwarzon da take nema kuma mai hannu da shuni ba talaka ba amma a Legas 


Ta ce dalilin wallafarta shine, dogaro da tayi da maganar nan da ke cewa, a rashin tayi a kan bar arha Wata budurwa 'yar Najeriya ta wallafa kyakyawan hotonta inda ta bayyana cewa tana nemawa kanta saurayi tare da kawarta. 


A wallafarta a shafinta na Twitter mai suna @adannanwaokolo, ta lissafa irin namijin da take so kuma ya miko kokon bararsa. 


Daya daga cikin yanayin mijin da take so shine ya kasance yana zama a tsibirin Legas, anguwar masu kudi ba ta talakawa ba. 


"Barkanku, ni da kawata muna bukatar samari. Dole ne ya zama dogo, baki, mai aiki mai kyau, gwarzo a gado, yana zama a tsibirin Legas ba unguwar talakawa ba, mai gemu, mai kawatacciyar murmushi, mai shekaru daga 25 zuwa 30," ta wallafa. 


Adanna ta bayyana cewa, dole ta sa ta fito ta yi wannan tallar saboda "A rashin tayi a kan bar arha."




A wani labari na daban, ba'a ritsa mako biyu ba da wata budurwa ta tsugunna har kasa don amsar zoben sa ranar auren ta, wata budurwa ma ta bi sahun ta. Wata budurrwa, Angel Nwedo, ta wallafa hoton sa ranar aurenta cikin farinciki. 


Maimakon saurayin ya tsugunna ya mika mata zobe kamar yadda aka saba, kawai sai ga budurwar a kasa tana amsar zoben cike da annashuwa. Wannan al'amarin yazo ne babu dadewa bayan hotunan wata budurwa mai suna Adaeza Gift Okolie, sun karade kafar sada zumunta. 


Maimakon saurayin ya tsugunna ya mika mata zobe kamar yadda aka saba, kawai sai ga budurwar a kasa tana amsar zoben cike da annashuwa. Wannan al'amarin yazo ne babu dadewa bayan hotunan wata budurwa mai suna Adaeza Gift Okolie, sun karade kafar sada zumunta. 


Source: Legit.ng


LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: 

0 Response to "Zukekiyar budurwa ta wallafa hotonta tana neman saurayi, ta ce kada talakan da ya kawo kansa "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?