--
Yanzu-yanzu: Masu zaben sarki sun aikewa gwamna El-Rufa'i sunayen mutane 3 (Kalli makin da kowanni ya samu)

Yanzu-yanzu: Masu zaben sarki sun aikewa gwamna El-Rufa'i sunayen mutane 3 (Kalli makin da kowanni ya samu)


Masu zaben sarki a masarautar Zazzau sun gabatar da sunayen mutane uku ga gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i domin zaban daya cikinsu matsayin sabon sarkin Zazzau, Daily Trust ta ruwaito. 

Ga sunayensu: 

Alhaji Bashir Aminu, Iyan Zazzau Ya samu maki 89, 


Alhaji Muhammed Munnir Jafaru, Yariman Zazzau, ya samu maki 87, 


da Alhaji Aminu Shehu Idris, Turakin Karamin Zazzau ya samu maki 53 . 


Yanzu haka masu zaben sarkin suna ganawa da gwamna El-Rufa'i a gidan Sir Kashin Ibrahim. Daily Trust ta tattaro cewa Yarimomi 11 suka bayyana niyyarsu na danewa kujerar sarautar kasar bayan rasuwar tsohon sarki, Alhaji Shehu Idris ranar Lahadi. 


Ba kowa zai iya neman kujeran Sarki ba Ba dukkan yan gidan sarauta ke iya takaran kujeran sarki ba, wadanda iyayensu ko kakkaninsu suka taba sarki ne za'a iya nadawa.


Source: Legit.ng


DAGA: 


LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: 
bzglobalservicelabari@gmail.com

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: 

0 Response to "Yanzu-yanzu: Masu zaben sarki sun aikewa gwamna El-Rufa'i sunayen mutane 3 (Kalli makin da kowanni ya samu) "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?