--
Tabdijam: Yadda jami'ai suka yi wa matashiya fyade a motar kaita asbiti bayan kamuwa da korona.

Tabdijam: Yadda jami'ai suka yi wa matashiya fyade a motar kaita asbiti bayan kamuwa da korona.

Wasu direbobin motar daukar marasa lafiya sun yi wa budurwa mai shekaru 19 fyade yayin da suka je har gida suka dauketa domin wucewa da ita aisbiti saboda kamuwa da cutar korona da tayi.

An gano cewa, wani matashi ne mai suna Noufal mai shekaru 29 a yayin da suke kan hanyar cibiyar killacewa ta Pathanamthitta da ke yankin Kerala a India, a ranar Asabar, 5 ga watan Satumba.

An kama Noufal a ranar Lahadi da safe, 6 ga watan Satumban 2020 bayan da wacce lamarin ya faru da ita ta sanar da ma'aikatan asibitin a kan abinda ya faru.


Bayan an kama shi, 'yan sanda sun ce basu ga wani lasisi ko takardar da ta bayyana shi cikin jami'ai ko direbobin motar da aka dauko budurwar ba.

Ministan lafiya na kasar, KK Shailaja, ya kwatanta lamarin da rashin tausayi tare da rashin imani.

Wani jami'i a sashin kiwon lafiya, ya sanar da jaridar The Indian Express cewa ,direba daya kadai ake tura wa dauko marasa lafiya domin gujewa mu'amalar marasa lafiyar da ma'aikatan.

Jami'in ya ce: "Bangaren direban an yi masa shinge kuma babu ma'aikacin lafiya ko na jinya da ke raka direban domin dauko marasa lafiya.


"Ana yin hakan domin karanta yawan jami'an lafiya da za su yi mu'amala da majinyatan. A lokuta kadan ne muke tafiya da ma'aikatan jinya."

A wani labari na daban, wani tsoho mai shekaru 67 wanda ya shiga hannun 'yan sanda bayan da ake zarginsa da yi wa yarinya mai shekaru 12 fyade, ya musanta yawan yadda ake ikirarin ya kwanta da ita.

Tsohon ya jaddada cewa sau daya ya taba lalata da ita, amma an ce sau hudu ne bayan babu gaskiya a lamarin, jaridar Daily Trust ta wallafa.

Tsohon mai suna James Olajoyetan, ana zarginsa da fara lalata da karamar yarinyar tun bayan da ta je hutun babbar sallah wurin kakanta makaho mai zama a yankin Ejigbo a jihar Legas.

'Yan sandan sun zargi Olajoyetan, wanda matukin adaidaita sahu ne, da lalata da yarinyar a dakin kakanta, sannan yana toshe mata baki saboda kada tayi ihun da zai sa kakan nata ya gane.

'Yan sandan yankin Ejigbo sun damke wanda ake zargin a ranar Asabar da ta gabata, bayan da ya kira yarinyar domin ya aiketa amma sai ya fara lalata da ita.

Source: Legit.ng

DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:
https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

SAYI  KWAKWKWARAR  DATAR MTN  MAI KYAU DA INGANCI ANAN DOMIN SIYA YANZU LATSA NAN↓↓↓
https://paystack.com/pay/mz-st-fdub

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 
https://www.bzglobalservice.com.ng/

KU BIYOMU A SHAFUKAN

@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/

@TWITTER: https://twitter.com/bzglobalsevice

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Tabdijam: Yadda jami'ai suka yi wa matashiya fyade a motar kaita asbiti bayan kamuwa da korona."

Post a Comment

Tell us what you think about this article?