--
Hisba Ta Kama Mabarata 648 A Kano

Hisba Ta Kama Mabarata 648 A Kano

Hukumar Hisba ta Jihar Kano ta kama akalla mutum 648 da ake zargin mabarata ne a titunan daban-daban na garin Kano daga watan Fabrailu zuwa yanzu.

Mai magana da yawun hukumar, Lawan Ibrahim, ya ce wadanda ake zargin an kama su ne a titunan Bata da Murtala Muhmamed da Asibitin Nasarawa da hanyar jirgin kasa da kuma Titin Yahuza Suya a cikin garin Kano. Mata 416 ne da kuma maza 232 aka kama.

Ibrahim ya ce hukumar za ta ci gaba da kama masu bara da suka ki bin dokar hana bara da gwamnatin ta saka.

“Za mu tabbatar da hana bara a titunan Kano.

“An kuma tantance wadanda aka kama, haka kuma wanda aka samu laifinsu ne na farko za a mika su wajen ‘yan uwansu.

“Wadanda kuma suka saba yi za mu kai su kotu”, inji shi, kamar yadda kamfanin dillacin labarai na NAN ya ruwaito.

Source: Aminiya Daily Trust

DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:
https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

SAYI  KWAKWKWARAR  DATAR MTN  MAI KYAU DA INGANCI ANAN DOMIN SIYA YANZU LATSA NAN↓↓↓
https://paystack.com/pay/mz-st-fdub

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 
https://www.bzglobalservice.com.ng/

KU BIYOMU A SHAFUKAN

@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/

@TWITTER: https://twitter.com/bzglobalsevice

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Hisba Ta Kama Mabarata 648 A Kano"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?