--
Yadda matata da aure da komai ta gudu wajen tsohon saurayinta take kwanciya da shi – Miji ya koka

Yadda matata da aure da komai ta gudu wajen tsohon saurayinta take kwanciya da shi – Miji ya koka

Wani mutumi dan kasar Afrika ta Kudu ya hau shafinsa na Twitter, inda yake bayyana labarin shi mai ban tausayi akan yadda ya rabu da matarsa da suka yi aure tsawon shekara biyu.

Mutumin mai suna @DMlamla, ya ce shi da tsohuwar matar tashi sunyi soyayya tsawon shekaru bakwai, kuma sunyi aure tsawon shekara biyu, sai ya fara ganin canji a wajenta a lokacin da ta samu aiki. Daga baya ya gano cewa tana zuwa wajen tsohon saurayinta. Kokarin da yayi wajen jawo hankalinta gare shi ya tafi a banza, saboda ta sanar da shi cewa har yanzu tana son tsohon saurayin nata, kuma shine dama wanda take so tun asali.

Ga dai abinda ya ce:

“Labarin rabuwa ta da matata. Mun yi shekara 7 muna soyayya, sannan muka yi aure na tsawon shekara biyu. Ta samu aiki, kawai sai na fara ganin canji a wajenta.

“Na kamata sama da sau uku ita da tsohon saurayinta, amma ta cigaba da cewa sun rabu, nayi kokarin daidaita abubuwa tsakanina da ita, amma abu bai yiwu ba. Na kira iyayena suma basu samu damar shawo kanta ba.

“Daga baya ta sanar dani cewa zai yi wuya ta iya rabuwa da shi saboda tana matukar son shi. Dalilinta shine tayi aure da wuri, kuma suna matukar son junansu da tsohon saurayinta hakan ya sanya baza su iya rabuwa ba.

“Hankalina ya tashi sosai, wannan shine karo na farko dana fara yiwa mace kuka a rayuwata, bazan manta yadda na durkusa ina rokonta akan ta yi hakuri ba.

‘Abinda ya sanya na yanke shawarar rabuwa da ita shine, lokacin da ta gaya mini cewa dama can tsohon saurayinta shine mijin da take mafarki, kawai ni dai ta san mutum ne mai kirki, amma zaman da take yi dani kawai zama ne take yi na hakuri.

‘Kawai dai abinda na sani shine baza ka taba yin daidai ga mutumin da ba naka ba.”


SOURCE: PRESSLIVES.COM

DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:
https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

SAYI  KWAKWKWARAR  DATAR MTN  MAI KYAU DA INGANCI ANAN DOMIN SIYA YANZU LATSA NAN↓↓↓
https://paystack.com/pay/mz-st-fdub

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 
https://www.bzglobalservice.com.ng/

KU BIYOMU A SHAFUKAN

@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/

@TWITTER: https://twitter.com/bzglobalsevice

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Yadda matata da aure da komai ta gudu wajen tsohon saurayinta take kwanciya da shi – Miji ya koka"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?