--
Na tafi karuwanci Dubai amma na kare a Mali -Matashiyar Budurwa

Na tafi karuwanci Dubai amma na kare a Mali -Matashiyar Budurwa




Wata matashiya mai shekara 21, Irhobisa Lawrence Orhumnzie, ta koka da yaudarar da magajiyar ta yi mata na kai ta karuwanci Dubai amma suka kare a kasar Mali.

Orhumnzie, ta yi wannan bayanin ne bayan hukumar IOC ta kwaso su zuwa Najeriya bayan sun makale a Mali sakamakon annobar COVID-19.

Orhumnzie wadda tana cikin mutum 109 da aka kawo Filin Jirgi na Murtala Mohammed da ke Legas ta ce an tafi da ita yawon karuwancin ne tare da wasu ‘yan mata 24, da sunan za a kai su Dubai.

“Mun tashi daga Legas, muka ratsa Kwatano da Jamhuriyar Benin da Togo, daga nan muka shiga kasar Mali.

” Muna shiga Bamako, ‘yan sandan Mali suka damke mu, suka tambaye mu ko za mu koma Najeriya muka ce, eh.

“Daga nan suka kai mu ofishin jakadancin Najeriya da ke Mali amma ba a samu damar maido mu ba saboda COVID-19. Sai yanzu IOC ta taimaka muka dawo”, inji ta.


SOURCE:https://aminiya.dailytrust.com.ng/  

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Na tafi karuwanci Dubai amma na kare a Mali -Matashiyar Budurwa"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?