--
Dan shekara 70 ya yiwa yarinya ‘yar shekara 8 fyade ya bata N80 tayi shiru da bakinta

Dan shekara 70 ya yiwa yarinya ‘yar shekara 8 fyade ya bata N80 tayi shiru da bakinta



An kama wani mutumi dan shekara 70 da ake zargin ya yiwa wata karamar yarinya ‘yar shekara takwas fyade a Chanchanga dake garin Minna babban birnin jihar Neja.

Mutumin mai suna Mohammed Sani Umar (Tela) an kama shi da laifin yiwa yarinyar fyade har sau biyu kafin ya bata N80 domin tayi shiru da bakinta. Amma daga baya yarinyar ta tona mishi asiri bayan mahaifiyarta ta gano cewa akwai matsala a tare da ‘yar tan.

Da yake bayyana yadda lamarin ya faru, kawun yarinyar mai suna Abubakar ya sanarwa da Sahara Reporters: “Ta shafe makonni tana rashin lafiya, har yanzu ma bata samu sauki ba. Sai wata makwabciya ta bawa mahaifiyar yarinyar shawara akan ta sanya ido akan yarinyar.

“Bayan ‘yan kwanaki sai taga jini a jikin wandonta, sai take tambayarta mene ya faru.

“Yarinyar ta dauki mahaifiyarta zuwa inda mutumin yake, suna zuwa ta nuna shi da hannu.

“Yana ganin yarinyar da mahaifiyarta sai ya fara rokonsu akan su rufa masa asiri,” cewar Abubakar.

Ya kara da cewa Umar ya amsa laifinsa bayan ya ci uban bugu daga wajen wasu matasa na yankin, kafin su mika shi zuwa wajen ‘yan sanda domin cigaba da bincike.

“Mahaifiyar yarinyar ta fara kuka tana neman taimako. Inda mutane suka fara taruwa, suka shiga dashi wani gida suka yi masa dukan tsiya, sannan ya bayyana musu cewa yayi lalata da ita har sau biyu.

“Ya ce ya bata N50 da farko, sannan ya bata N30 a karo na biyu. Mun mika shi ga hannun ‘yan sanda domin a kai shi kotu a yanke masa hukunci,” Abubakar ya ce.

Iyayen yarinyar kuma sun roki ‘yan sanda da su tabbatar da anyi adalci wajen yanke hukunci, inda suka ce suna tsoron za a iya watsi da karar saboda Umar mutum ne da yake da alfarma a yankin.

DPO na ofishin ‘yan sandan ya ce za a kai karar gaban rundunar ‘yan sanda ta jiha a yau Litinin dinnan.

“Muna so ‘yan sanda su yi abinda ya kamata, saboda mutumin yana da alfarma sosai, kuma yana da mutane da suke belin mutanen da suka yi laifi aka kama su.

“Ya san manyan mutane a wannan yankin, akwai yiwuwar za su tsaya mishi su sanya ‘yan sanda su sake shi ayi watsi da lamarin.

“Tilas ‘yan sanda su tabbatar da adalci a wannan lamarin,” cewar iyayen yarinyar.


KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
 LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657


0 Response to "Dan shekara 70 ya yiwa yarinya ‘yar shekara 8 fyade ya bata N80 tayi shiru da bakinta"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?