--
Wata sabuwa: Wike ya tona asirin abinda shugaba Buhari ke shirin yi a zaben 2023

Wata sabuwa: Wike ya tona asirin abinda shugaba Buhari ke shirin yi a zaben 2023



Fara zancen zaben shekarar 2023 a wannan shekara ta 2020, yayi kusa da yawa, cewar gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Jaridar ta ruwaito cewa gwamnan ya bayyana haka ne a hira da yayi da gidan talabijin na Arise TV, kamar yadda yayi watsi da zargin da ake yi masa na cewa yana shirin fitowa takarar shugaban kasa a shekarar 2023.

Gwamnan jihar ta Rivers dai ya bayyana cewa babban abinda ke gaban shi a yanzu shine bunkasa jihar Rivers. A cewar shi fara shirin siyasar 2023 a wannan lokacin ka iya dauke masa hankali akan ayyukan da ya dauki alkawari zai yiwa mutanen jihar Rivers.

“Daga yaya zan fara zancen fitowa takarar shugaban kasa a shekarar 2023, bayan na san cewa har yanzu ina da abubuwan da ya kamata na yiwa jiha ta, hakan zai dauke mini hankali ne,” cewar shi.

Gwamnan jihar ta Rivers ya ce siyasar 2023, matsalar jam’iyyar APC ce, saboda ita ce akan mulki, ba wai matsalar PDP ba ce.

Ya cigaba da bayani cewa tunda shugaba Buhari zai bar kujera a shekarar 2023, dole ne wasu daga cikin ‘yan jam’iyyarsa za su so su hau kujerar shi.

Gwamnan jihar ta Rivers ya kara da cewa yana da tabbacin cewa shugaba Buhari ba zai taba bari jam’iyyarsa ta sha kasa ba a 2023.

Ya ce: “Shugaban kasa zai gama mulkinsa, saboda haka wasu za su so hawa kujerar shugaban kasar. A PDP kujerar wa kuke ganin za ku hau, babu wanda zaku hau kujerar shi.

“Mun gama mulki shekarun da suka gabata, kuma har kun fara zancen shugabancin kasa.

“Idan har haka ta faru, ba zaku iya tsayawa ku samarwa da mutanenku romon dimokuradiyya ba, kuma shine abinda yake faruwa yanzu a APC.

“Kowa yana tunanin karbar mulki daga hannun shugaban kasa. Maimakon ku tsaya kuyi aiki kun koma kuna tunanin karbar mulki.

“Har yanzu baku san zuciyar ‘yan Najeriya ba. Abin duba a nan shine, a matsayinta na jam’iyya mai mulki, da kuma shugaban kasa ba zai taba bari jam’iyyar shi ta fadi ba.”



KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
 LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Wata sabuwa: Wike ya tona asirin abinda shugaba Buhari ke shirin yi a zaben 2023"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?