--
Saudiyya za ta kori mutane miliyan 1.2 wadanda ba ‘yan kasar ba a cikin wannan shekarar

Saudiyya za ta kori mutane miliyan 1.2 wadanda ba ‘yan kasar ba a cikin wannan shekarar



A wata kididdiga da kamfanin Jadwa na kasar Saudiyya ya fitar, kimanin mutane miliyan daya da dubu dari biyu ne za su bar kasar saudiyya zuwa kasashen su daga nan zuwa karshen wannan shekarar.

Duk da wannan korar mutane wadanda ba ‘yan kasar ba da Saudiyyar za ta yi, matsalar rashin aikin yi za ta cigaba da zama a kashi 12 cikin dari daga nan zuwa karshen wannan shekarar.

A rahoton da kamfanin na Jadwa ya fitar, ma’aikatun da wannan lamari zai shafa sun hada da asibitoci, wuraren sayar da abinci, kamfanonin tafiye-tafiye, kamfanonin tsaro, da kuma kamfanoni na gine-gine.

Duk da cewa an kasar na kokarin cire dokar hana zirga-zirga, amma wasu wuraren za su dauki lokaci kafin su cigaba da aiki, irinsu otel-otel, kamfanonin sufuri, wuraren sayar da abinci, wuraren shakatawa, da kuma wuraren nishadi.

Haka rahoton ya bayyana cewa hukumomin kasar sun sanar da cewa ‘yan kasar za su cigaba da rike ayyukansu kamar yadda suka saba, inda ya zuwa yanzu kasar ta Saudiyya ta biya kimanin Riyal biliyan 2.4 ga marasa karfi a kasar domin tallafa musu a wannan lokaci.

Da wannan yawan mutane da ake shirin kora a kasar, akwai dama sosai ga mutanen kasar wajen samun ayyukan yi. Yayin da gwamnatin kasar ta dakatar da bawa mutane Visa.


KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Saudiyya za ta kori mutane miliyan 1.2 wadanda ba ‘yan kasar ba a cikin wannan shekarar"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?