--
Ko ina akwai na Allah: Wani mutumi ya mayar da N1.8m da ya tsinta a cikin kwalin Indomie da ya siya

Ko ina akwai na Allah: Wani mutumi ya mayar da N1.8m da ya tsinta a cikin kwalin Indomie da ya siya



Wani dan Najeriya da aka bayyana sunan shi da Mr Chidiebere Ogbonna, ya mayar da naira miliyan daya da dubu dari takwas (N1.8m), wanda ya tsinta a cikin kwalin indomie da ya siya.

A yadda rahoton ya nuna, kwalin Indomie din an saka Indomie din kadan a ciki, inda sauran kuma aka cika da kudi ‘yan naira 1000.

Chidiebere ya ce bayan ya isa gida, ya bude kwalin Indomie din, yana ganin abinda ke ciki yayi gaggawar mayar da kudin zuwa wajen da ya siyo Indomie din.

Da aka tambayeshi dalilin da ya sanya ya dawo da kudin duk da wannan matsalar tattalin arziki da wahala da ‘yan Najeriya suke ciki, sai ya ce kudin ba nashi bane, saboda haka bashi da wani dalili da zai saka ya ajiye cinye kudin.

Mai shagon da ya sayi Indomie din wanda ya cika da farin ciki, yayi masa godiya, sannan yace masa ya dinga zuwa yana karbar Indomie a shagon a duk lokacin da yake bukata, daga wannan lokacin har zuwa watan Disambar wannan shekarar.

To dama dai ance ko ina akwai na Allah, domin kuwa ba duka ne aka taru aka zama daya ba.

 KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
 LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Ko ina akwai na Allah: Wani mutumi ya mayar da N1.8m da ya tsinta a cikin kwalin Indomie da ya siya"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?