--
Da dumi-dumi: Jami'an NCDC sun fitittiki dalibai yayinda suka koma makaranta yau

Da dumi-dumi: Jami'an NCDC sun fitittiki dalibai yayinda suka koma makaranta yau

Jami'an hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya watau NCDC sun fitittiki daliban makarantar West African People’s Institute (WAPI) da suka isa makaranta domin shiga aji. Hakan ya faru ne da safiyar yau Talata, 16 ga Yuni, 2020 a jihar Cross River. Daily Trust ta ruwaito.

Za ku tuna cewa gwamnan jihar CrossRiver, Farfesa Ben Ayade, a makon da ya gabata ya bada umurnin bude makarantu uku a fadin jihar. Sauran makarantu biyun sune makarantar sakandaren gwamnati Egola, da kuma makarantar sakandaren gwamnati Ikom. Daliban yanzu na wajen makarantar WAPI a Calabar. Jihar Cross River ce jihar daya tilo da ba'a samu bullar cutar Coronavirus ba har yanzu.


Ku saurari cikakken rahoton.....

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Da dumi-dumi: Jami'an NCDC sun fitittiki dalibai yayinda suka koma makaranta yau "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?