--
Ƙungiyoyin farar hula 16 za su sa ido kan yadda za a kashe kudin Abacha

Ƙungiyoyin farar hula 16 za su sa ido kan yadda za a kashe kudin Abacha

ROHOTON: BBCHAUSA

A yau ne gwamnatin Najeriya ta rufe karbar takardun ta yi daga kungiyoyin farar-hula, wadanda ke sha`awar aiki da gwamnati wajen sa-ido a kan yadda za ta kashe wani kudi, fiye da dala miliyan 300 da ake zargin an sace a zamanin gwamnatin Sani Abacha.

A watan Afirilun da ya wuce ne gwamnatin Najeriya ta samu damar karbo kudin daga Amurka, bayan sun kulla wata yarjejeniya, ciki har da sanya kungiyoyin farar-hula da za su bi diddigin yadda za a kashe kudin.

Kungiyoyin farar-hula 16 ne suka nuna sha'awar aiki kafada-da-kafada da gwamnatin Najeriyar wajen sa-ido a kan yadda za ta kashe kudin daga ta karbo daga Amurka, dala miliyon 311.

HAkan na zuwa ne bayan da suka cimma yarjejeniya da gwamnatin Amurkan da ta Island of Jersey, cewa za a yi amfani da kudin ne wajen ci gaba da gina wasu hanyoyin mota tagwaye, da suka tashi daga Legas suka dangane da Ibadan, da wadanda suka tashi daga Abuja suka dangana da Kano da kuma gadar motar nan da aka fi sani da second Niger Bridge da ke kudancin Najeriya... sannan wajibi ne a sanya kungiyoyin a cikin masu sa ido.

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com


KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANANhttps://www.bzglobalservice.com.ng/



KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Ƙungiyoyin farar hula 16 za su sa ido kan yadda za a kashe kudin Abacha"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?