--
Covi-19: Ma'aikatan lafiya 47 ne suka kamu da cutar korona a Kano

Covi-19: Ma'aikatan lafiya 47 ne suka kamu da cutar korona a Kano

ROHOTON: https://www.bbc.com/hausa/

Akalla ma'aikatan lafiya 47 ne a Kano suka kamu da cutar korona kamar yadda gwamnatin jihar ta sanar.

Babban jami'i a kwamitin da gwamnatin jihar ta kafa domin yaki da cutar korona, Dr Tijjani Hussain ne ya tabbatar da hakan yayin wani jawabi ga manema labarai ranar Lahadi.

Dr Tijjani ya ce an tabbatar da kamuwar ma'aikatan lafiyar da cutar ne a 'yan makonni da suka gabata, inda ya ce ba a samu karin wani ma'aikacin lafiyar da ya sake kamuwa ba.

Jihar Kano ce dai jiha ta biyu a jerin jihohin da ke da yawan adadin masu dauke da cutar korona a Najeriya.

Adadin mutanen da aka tabbatar sun harbu da cutar korona a Jihar Kano da ke arewacin Najeriya sun kai 602, a cewar ma'aikatar lafiya ta jihar.

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANANhttps://www.bzglobalservice.com.ng/

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Covi-19: Ma'aikatan lafiya 47 ne suka kamu da cutar korona a Kano"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?