--
Yanzu yanzu: INEC Ta Soke Wasu Runfunan Zaɓe 746 a Faɗin Najeriya

Yanzu yanzu: INEC Ta Soke Wasu Runfunan Zaɓe 746 a Faɗin Najeriya


Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta bayyana cewa ta soke wasu runfunan zaɓe 746 dake faɗin Najeriya,


waɗanda mafi yawancin su a wurin bauta, gidan sarauta da kuma wuri mai zaman kanshi suke, kamar yadda vanguard ta ruwaito. 


Shugaban INEC, Farfesa Mahmud Yakubu, shine ya faɗi haka ranar Laraba a Abuja, a wurin taron da hukumar ke gudanarwa da kwamishinonin zaɓe RECs. 


Daga runfunan zaɓen 119, 973 da ake da su, Farfesa Yakubu yace yanzun akwai runfunan zaɓe 176, 846 a faɗin Najeriya, kamar yadda the nation ta ruwaito. 


Shugaban INEC ɗin yace an samu wannan ƙarin ne bayan wata kwaskwarima da hukumar ta gudanar a faɗin runfunan zaɓen dake ƙasar nan. 


Cikakken bayani zai zo daga baya 


Source: Legit 


DAGA BZ NEWS 24/7

0 Response to "Yanzu yanzu: INEC Ta Soke Wasu Runfunan Zaɓe 746 a Faɗin Najeriya "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?