--
Sojojin Najeriya za su yaƙi masu yaɗa farfaganda a kafofin sada zumunta

Sojojin Najeriya za su yaƙi masu yaɗa farfaganda a kafofin sada zumunta


Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana aniyarta ta ƙaddamar da Atisayen Murmushin Kada karo na shida, wanda a turance aka fi sani da Crocodile Smile.


Sai dai a wannan karon, atisayen zai mayar da hankali ne wurin bin diddiƙi da kuma gano masu watsa farfagandar ƙarya a shafukan sada zumunta.


A wata sanarwa da mai magana da yawun sojojin ƙasar Kanal Sagir Musa ya fitar, ya bayyana cewa wannan ne atisaye na farko makamancin haka da za a gudanar a tarihin sojoji a Afrika.


Ya kuma bayyana cewa wannan atisayen na murmushin kada zai sa ido ga 'yan Boko Haram da ke guduwa daga arewa maso gabashin ƙasar zuwa sauran sassan Najeriya domin gano su.


Za a ƙaddamar da atisayen ne a ranar 20 ga watan Oktoba zuwa 31 ga watan Disambar 2020.


Source: Bbchausa


LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A WHATSAPP:

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A TELEGRAM:


KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app75765


0 Response to "Sojojin Najeriya za su yaƙi masu yaɗa farfaganda a kafofin sada zumunta"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?