--
’Yan Arewa Sun Nuna Wa IPOB Yatsa Kan Kisan Hausawa A Ribas

’Yan Arewa Sun Nuna Wa IPOB Yatsa Kan Kisan Hausawa A Ribas

Kungiya kare yankin Arewacin Najeriya (CNG) ta yi Allah-wadai da harin da kungiyar ’yan awaren Biyafara ta IPOB ta kai wa al’ummar Hausawa a Karamar Hukumar Oyigbo ta Jihar Ribas da ya yi sanadiyyar kashe mutum biyu.

CNG a sanarwar da kakakinta, Abdul’Aziz Suleiman ya fitar ranar Talata a Kaduna, ta yi gargadin cewa dole ne kowace al’umma ta girmama baki da ke zaune a yankinta a matsayinsu na ’yan kasa.

Ta kuma ce, “Yayin da muke jiran rahoto daga shugabannin ’yan Arewa a Jihar Ribas, muna kara tabbatar wa ’yan Arewa mazauna kowanne sashe na Najeriya cewa ba za mu lamunci cin kashin da ake musu ba.

“Ita kuwa kungiyar IPOB, irin yadda take cin karenta ba babbaka ta hanyar shirya taruka a bainar jama’a ba tare da shayin kowa ba da shirya zanga-zanga, yin barazana tare da aiwatar da abin da ta fada a cikinta, alamace ta irin raunin tsaro da kuma tabbatar da doka da oda a kasa.

“Abin takaici ne yadda Gwamnatin Tarayya da hukumomi a Kudancin Najeriya suka kawar da kai suka kyale kungiyoyi irin IPOB na ci gaba da cin karensu ba babbaka.

“Hakan tarnaki ne ga kokarin gina kasar da kowane dan Najeriya zai zauna a inda yake da bukata.

“Karancin abin da muke bukata shi ne kowane gwamnan Kudu ya fito ya magantu kan hakkin ’yan Arewa na zama ba tare da an kyamace su ba, a tabbatar da ’yancinsu na yin addini, sana’a, adalci da kuma kare su”, inji kungiyar.

Daga nan suka tunatar da jama’a cewa dokar kasa ta tanadai ’yancin zama tare da yin walwala a kowane yanki ba tare da tsangwama ko nuna kyama ba.

Source: Aminiya Daily Trust

DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:
https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

SAYI  KWAKWKWARAR  DATAR MTN  MAI KYAU DA INGANCI ANAN DOMIN SIYA YANZU LATSA NAN↓↓↓
https://paystack.com/pay/mz-st-fdub

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 
https://www.bzglobalservice.com.ng/

KU BIYOMU A SHAFUKAN

@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/

@TWITTER: https://twitter.com/bzglobalsevice

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "’Yan Arewa Sun Nuna Wa IPOB Yatsa Kan Kisan Hausawa A Ribas"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?