--
Masu Garkuwa Sun Kashe Jami’in DSS A Jihar Katsina

Masu Garkuwa Sun Kashe Jami’in DSS A Jihar Katsina


Masu ta’adar garkuwa da mutane sun kashe wani jami’in hukumar tsaron ta farin kaya (DSS), Sadiq Abdullahi Bindawa, a jihar Katsina.

Marigayi Sadiq ya yi gamo da karshensa a hannun ‘yan ta’addan bayan sun karbi naira miliyan 5 na kudin fansa ta garkuwar da suka yi da shi.

Tun da farko lamarin ya faru ne a ranar Asabar yayin da masu garkuwar suka kai masa takakakka awanni kadan bayan shigarsa gida yayin da ya tafi hutun karshen mako daga Abuja zuwa Katsina.

Maharan sun yi awon gaba da shi sannan kuma suka bukaci naira miliyan 25 a matsayin kudin fansa.

Abokan aikin mamacin sun yi wa masu garkuwar kwanton bauna a inda suke shirin karbar kudin fansa, lamarin da ya janyo musayar wuta a tsakaninsu.

A yayin da a nan ajali ya cimma wasu daga cikin masu garkuwar, ‘yan kalilan da suka tsere suka koma suka harbe Sadiq tare da barin gawarsa a dokar daji.

Majiyarmu ta ce an yi jana’izarsa a safiyar yau ta Talata bisa koyarwar addinin Islama.

Source: Aminiya Daily Trust


LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 


KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Masu Garkuwa Sun Kashe Jami’in DSS A Jihar Katsina"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?