--
Magidanci Ya Farke Cikin Matarsa Don Gano Abin Da Za Ta Haifa

Magidanci Ya Farke Cikin Matarsa Don Gano Abin Da Za Ta Haifa


Wani magidanci a kasar Indiya ya farke cikin matarsa mai juna biyu domin ya ga abin da za ta haifa namiji ne ko mace.


Mutumin mai suna Pannalal, ya shiga hannun ’yan sanda bayan faruwar lamarin a Jihar Uttar Pradesh da ke Arewacin Indiya.


Jami’in ’yan sanda PravinSingh Chauhan ya shaida wa kafafen watsa labarai cewa matar tana cikin mawuyacin hali sakamakon raunin da mijin ya yi mata.


Ya ce “Yanzu muna bincikar dalilin da ya sa mijin ya aikata wannan danyen aiki.”

Dangin matar sun ce mijin yana da ’ya’ya mata 5 don haka yake tsananin son ya haifi namiji.

Sun ce mijin ya farke cikin matar ce don ya tabbatar da ko tana dauke da namiji a wannan karo.

Gidan Talabijin na NDTV ya ruwaito cewa matar tana dauke da cikin wata bakwai ne lokacin da mijin ya farke ta.

Duk da yadda gwamnati take ta kokarin wayar da kan jama’a, har yanzu a Indiya an fi fifita samun ’ya’ya maza a kan mata.

Mafi yawan mutanen Indiya sun fi ganin ’ya’ya maza a matsayin jari inda suke kallon mata a matsayin nauyi da wahala.

A shekarar 2018 an fitar da rahoton daake bayyana cewa duk shekara ana rasa ’ya’ya mata miliyan biyu sakamakon zubar da cikinsu da ake yi a qasar Indiya.

Zaben cikin da ake so a haifa na ci gaba da kamari sakamakon rashin doka mai karfi da za ta shawo kan matsalar.

“Muna sane da zaven abin da za a haifa kuma lamarin yana matuqar karuwa,” inji wani jami’in gwamnati.

“Wannan alamari na kyamatar ’ya’ya mata ya shafi daukacin mutanen Indiya ne,” inji rahoton.


Source: Aminiya Daily Trust

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: 

0 Response to "Magidanci Ya Farke Cikin Matarsa Don Gano Abin Da Za Ta Haifa"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?