--
Masu yada kalaman batanci za su biya tarar miliyan 5

Masu yada kalaman batanci za su biya tarar miliyan 5


Ministan Yada Labarai Alhaji Lai Mohammed ya ce Hukumar Kula da Gidan Rediyo da Talabijin ta Najeriya (NBC) ta kara yawan tarar da za a ci duk gidan rediyo ko talabijin da ya ba da kafar yin kalaman batanci zuwa Naira miliyan biyar.

Ministan ya bayyana hakan ne a wajen bukin kaddamar da sabon kundin dokokin yada labarai bugu na shida ranar Talata.

Hukumar ta hukunta gidajen kafofin yada labarai 31 wadanda suka yi karya a game da COVID-19 da kalaman kiyayya da sauransu.

Alhaji Lai ya ce an yi karin tarar ne daga N500,000 zuwa miliyan biyar saboda rashin bin doka da gkafofin yada labaran suka yi yayin manyan zabukan shekarar 2019.

“A lokacin zaben na 2019, idan ’yan siyasa suka tunkari kafofin yada labarai da batancin da suke son yi a kan wasu aka ki sanyawa, sai su biya kudin da za a biya tarar ta N500,000 har da riba.
“Duk da miliyan biyar din da muka kara, idan kafar watsa labarai ta biya amma ba ta daina bayar da damar yin kalaman batanci ba, to ba mu da wani zabi sai mu kwace lasisin su”, inji shi.

Ya ce canje-canjen da aka samu a sabon kundin dokokin yada labaran dai sun fi yawa ta fannin harkokin siyasa da labaran gida da tallace-tallace da kuma hana gasa.

A baya dai an zargi gwamnati da yunkurin amfani da dokokin hana kalaman batanci don haramta wa masu suka da ’yan adawa damar fadin albarkacin bakinsu.

SOURCE: https://aminiya.dailytrust.com.ng/

DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG


KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN


KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Masu yada kalaman batanci za su biya tarar miliyan 5"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?