--
Rikici ya barke yayin da matar aure ta kama mijinta da yayarta wacce suke uwa daya uba daya suna lalata a otel

Rikici ya barke yayin da matar aure ta kama mijinta da yayarta wacce suke uwa daya uba daya suna lalata a otel

Wata mata mai shekaru 27 dake da ‘ya’ya guda uku ta koka a shafukan sadarwa, bayan ta kama mijinta yana lalata da kanwarta da suke uwa daya uba daya.

Da take bayyana yadda lamarin ya faru, ta ce ta kwashe shekara biyu tana samun matsala da mijinta saboda wata mata da yake hira da ita a waya.

Ta ce ta sha samun shi tayi masa magana game da matar, amma sai dai ya bata hakuri ya kuma yi mata alkawarin ba zai kara kula matar ba.

Ta ce har iyayenta ta sanarwa dangane da lamarin, babbar yayarta ta bata shawara akan tayi hakuri tunda dai har yana kula da ita yadda ya kamata.

Kwanan nan sai ta gano cewa mijin nata ya cigaba da kula matar, sai ta yanke shawarar gano abinda yake yi da inda suke haduwa.

Sai ta bishi wani otel da suke haduwa, tana zuwa sai ta ga cewa ashe yayarta ce take kwanciya da mijinta.

Ashe ta sayi sabon layi ne wanda take hira da shi daya kawai, duk cikinmu babu wanda yake da wannan lambar.

Ta ce ta sha kuka har ta gaji, inda ta ce tana tunanin za ta hakura da auren, za ta kyale mijin nata yaje ya auri yayarta.

Ta ce sun jima suna bata hakuri akan kada ta fito da maganar.

SOURCE: PRESSLIVES.COM


KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
 LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Rikici ya barke yayin da matar aure ta kama mijinta da yayarta wacce suke uwa daya uba daya suna lalata a otel"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?