--
Matar da ta kware wajen saye da sayar da jarirai ta shiga hannu yayin da take cinikin wani sabon jariri

Matar da ta kware wajen saye da sayar da jarirai ta shiga hannu yayin da take cinikin wani sabon jariri


An kama wasu mata guda biyar a lokacin da suke cinikin sayar da wani sabon jariri da aka haifa mako biyu da suka wuce.

An kama Mrs Roseline Nwokocha daga Umuahia tare da ‘yar uwarta, Chioma, a Fatakwal, jihar Rivers. Chioma dai ta raka ta ne don ta ga jaririn, kamar yadda Roseline ta sanar da ‘yan sanda.

Wannan dai ba shine karo na farko ba, ta ce. Ta ce zuwanta na karshe da ta je Fatakwal sayen jaririn, ‘yar uwartan ta rakota saboda a lokacin bata jin dadi.

Jaririn karshe da ta saya ta biya naira miliyan daya da dubu dari daya (N1.1m), a lokacin da ake tambayar ta, ta ce jaririn da take kokarin siya suna yin ciniki ne akan naira miliyan daya, inda ta ce tana so ita kuma ta sayar da shi ta samu ribar dubu dari.

An same ta da naira miliyan daya da dubu dari daya a cikin jaka, inda ta ce wanda zai sayi jaririn ne ya bata kudin a lokacin da ta baro Umuahia.

Da aka tambayeta wanda take shirin bawa kudin sai ta nuna wata mata a cikin kungiyar ta su mai suna Chi Chi. Da aka tambayi Chi Chi inda take kokarin samo jaririn sai ta nuna wata mata mai suna Aunty Ify. Ta ce Aunty Ify ta same ta inda ta bayyana mata cewa tana da jariri na sayarwa akan naira dubu 950, ita kuma sai ta dora ribar dubu hamsin ta sayarwa da Mrs Nwokocha akan naira miliyan daya. Ta ce idan Mrs Nwokocha ta bata kudin za ta bawa Aunty Ify kasonta, inda ita kuma Aunty Ify za ta kawo jaririn.

Da aka tambayi Aunty Ify inda ta samo jaririn da za ta sayar, ta ce ita ma bata sani ba. Ta ce ita ma wasu ne suka kira ta a waya cewa suna da jariri da za su sayar.

An tambayi Mrs Roseline Nwokocha abinda tayi da jaririn da ta sayar mako biyu da suka wuce, sai ta ce jaririn yana Aba tare da wasu ma’aurata. Da aka tambayeta sunayen ma’auratan ta kasa bayar da amsa.

Haka kuma an tambayeta mai take shirin yi da jaririn da ta zo za ta siya, sai ta ce wasu ma’aurata ne a Umuahia za su raini yaron. Haka suma ma’auratan na Umuahia ta ce ba ta san sunayensu ba.

Mace ta biyar a cikin kungiyar ita ce mahaifiyar jaririn da Mrs Nwokocha ta saya a wurinta mako biyu da suka wuce.

Ga dai bidiyon mutanen a lokacin da suke amsa laifinsu:
View this post on Instagram

Five women who specialize in buying and selling babies were nabbed in Port Harcourt while negotiating the sale of a two-week-old baby. . . Mrs Roseline Nwokocha from Umuahia was arrested with her sister, Chioma, at Rumuokuta junction in Port Harcourt, Rivers State. Chioma had accompanied her to Rivers State to see the baby, she said. . . It isn't her first time, she revealed. She said the last time she came to Port Harcourt to buy a baby, her sister Chioma accompanied her because she was sick. . . The previous child she bought cost her N1.1 million, she revealed during interrogation. The child she was nabbed trying to buy was to be sold at N1 million and she said she planned to give the child to the buyers at N1.1 million Naira. . . She was nabbed with the N1.1 million Naira in cash, and stated that it was the buyers who gave her the money as she left Umuahia for Port Harcourt. . . When asked who she planned to pay the money to, she pointed at another woman in the group named Chi Chi. Chi Chi was asked who she planned to get the baby from and she pointed to another woman named Aunty Ify. She said Aunty Ify approached her that she had a baby for sale at 950,000 Naira so, she topped her gain of 50,000 Naira and sold to Mrs Nwokocha at 1 million Naira. She said once Mrs Nwokocha's money is handed to her, she will hand Aunty Ify's share to her and Ify will then bring the baby. . . Aunty Ify was asked where she got the baby she wanted to sell from and she said she has no idea. She said someone called her that they had a baby to sell so she set the wheels in motion. . . Mrs Roseline Nwokocha was asked what happened to the baby she bought two weeks ago and she said the baby is in Aba with a couple. She was asked for the couple's name but she couldn't provide an answer. She was also asked what she planned to do with the baby she came to buy before she was nabbed and she said a couple from Umuahia were to adopt the child. She also said she couldn't remember the Umuahia couple's name. . A 5th woman in the group was identified as the mother of the previous baby Mrs Nwokocha bought.

A post shared by Lindaikejiblog (@lindaikejiblogofficial) on


 KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
 LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Matar da ta kware wajen saye da sayar da jarirai ta shiga hannu yayin da take cinikin wani sabon jariri"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?