--
Da duminsa: Iya ‘yan kasar Saudiyya ne kawai za su yi aikin Hajjin bana – Gwamnatin Saudiyya

Da duminsa: Iya ‘yan kasar Saudiyya ne kawai za su yi aikin Hajjin bana – Gwamnatin Saudiyya

Gwamnatin kasar Saudiyya ta bayyana cewa aikin Hajji na wannan shekarar da za ayi a wata mai zuwa, iya mutane kalilan ne za a bari su samu halarta.

Ta kuma ce wadanda za su halarci aikin Hajjin za su zamo daga kasashe daban-daban, amma kuma iya wadanda ke zaune a cikin kasar a yanzu.

Ma’aikatar aikin Hajji da Umrah ta kasar ta bayyana haka a ranar Litinin, inda ta ce ta dauki wannan mataki ne saboda annobar coronavirus da ake fama da ita.

Ma’aikatar ta ce ta yanke shawarar hakan ne bisa la’akari da ganin har yanzu cutar na cigaba da yaduwa cikin al’umma, kuma tana iya kamari a wajen da mutane suka taru da yawa.

“Iya mutane kalilan ne wadanda suke zaune a kasar Saudiyya za a bari suyi aikin Hajji.

“Mun yanke wannan shawara ne don tabbatar da cewa anyi aikin Hajji lafiya an gama lafiya ta hanyar bin duka dokokin da suka dace,” cewar ma’aikatar ta aikin Hajji da Umrah.

A shekarar da ta gabata mutane miliyan 2.5 ne dai suka gabatar da aikin Hajji a kasar ta Saudiyya.

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Da duminsa: Iya ‘yan kasar Saudiyya ne kawai za su yi aikin Hajjin bana – Gwamnatin Saudiyya"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?