--
Coronavirus: Iran za ta bude masallatai saboda goman karshe

Coronavirus: Iran za ta bude masallatai saboda goman karshe

Iran za ta sake bude dukkanin masallatan kasar a yau Talata a wani mataki na sasauta dokar kulle.

Rahotanni sun ce aa a bude masallatan na kwanaki uku ne kawai domin samun damar ibada a cikin dare masu daraja na watan Ramadan. sannan za a bayar da damar ibadar ne kawai na tsawon sa'a biyu, sannan mutane za su sanya takunkumi da safar hannu da kuma bai wa juna tazara.

Watanin biyu da suka gabata aka rufe masallatai a kasar lokacin da aka soma samun barkewar cutar korona, ko daya ke a makon daya gabata an sake bude wasu masallatai amma a yankunan da cutar ba ta yadu sosai ba.

Ma'aikatan Lafiya sun sha gargadi cewa dage dokokin yakar wannan annoba a yanzu ka iya jefa al'ummacikin wata sabuwar barazanar barkewar cutar.

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANANhttps://www.bzglobalservice.com.ng/

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Coronavirus: Iran za ta bude masallatai saboda goman karshe"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?