--
Allah ya yi wa jarumin Kannywood Ubale Ibrahim rasuwa

Allah ya yi wa jarumin Kannywood Ubale Ibrahim rasuwa



Allah ya yi wa daya daga cikin jaruman masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, Ubale Ibrahim wanda aka fi sani da wanke wanke rasuwa. Jarumin ya rasu ne a daren ranar Alhamis, 30 ga watan Afrilu. Za a yi jana’izar marigayin a yau Juma’a, 1 ga watan Mayu, da karfe 8:00 na safe a Rangaza bayan gidan man Chalawa, kamar yadda jarumi Sani Danja ya wallafa a shafinsa na Instagram.

 Mutuwar Ubale na zuwa ne a daidailokacin da ake tsaka da yawan mace-mace na ban mamaki a jahar Kano. Tuni dai yan uwansa jarumai na masana’antar fim suka fara nuna alhini da yi masa addu’a a shafin Instagram. Ga wasu daga cikin jaruman da suka yi ta'aziyyar marigayin: Ali Nuhu ya wallafa a shafinsa: “Allah ya jikan Ubale Ibrahim, ya sa mutuwa hutu ce gareshi.”



Falalu A Dorayi ya wallafa a nasa shafin: “Innalillahi wainna ilaihi rajiun. Allah yayi wa UBALE IBRAHIM (wanke-wanke) Rasuwa. Yan uwa mu sanya shi a addua. Allah yai masa rahma.”




 Nuhu Abdullahi: “Allah ya gafarta maka Ubale, YA kuma yafe maka kura-kuran ka, YA sa aljannace makomar ka, amin.”




 Fati Abubakar: “Innalillahi wa'inna ilaihiraju'un Allah ya gafarta maka kura kuranka amin”



 A gefe guda mun ji cewa jama'ar Kano na zaune cikin fargaba saboda yawaitar mace - macen mutane, yawancinsu tsoffi, da ake samau a cikin birnin jihar. Tun a makon jiya gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya saka dokar kulle jihar Kano; ba shiga, ba fita, sannan jama'a ma ba za su fito daga gidajensu ba. Gwamnatin jihar ta dauki wannan tsatsauran mataki ne biyo bayan bullar annobar covid-19 a jihar.

Duk da gwamnatin Kano ta musanta labarin yawaitar mutuwar mutane a cikin birnin jihar, rahotanni sun bayyana cewa adadin mutanen da ke mutuwa ya na cigaba da karuwa. An samu mutuwar mutane da dama a cikin birnin Kano da kewaye daga yammacin ranar Juma'a zuwa ranar Asabar da rana. Fitattu daga cikin wadanda su ka mutu akwai:

tsohon kwamishina a jihar Kano; Farfesa Ibrahim Ayagi, editan jaridar Triump; Musa Ahmad Tijjani, tsohon shugaban hukumar ma'aikatan jihar Kano; Adamu Dal. Sauran sune: Nasiru Maikano Bichi, Musa Umar Gwarzo, Ustaz Dahiru Rabi'u, tsohon alkali; Khadi Salisu Lado, Nene Umma, Garba Sarki Fagge, Salisu Lado, Shamsiyya Mustapha, Nene Umma, Garba Sarki Fagge, Rabiu Dambatta, Kabiru Ibrahim Bayero da mahaifiyar fitaccen mawaki, Ado Gwanja.



KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com



KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/


KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: BZGLOBALSERVICE.COM.NG APP

0 Response to "Allah ya yi wa jarumin Kannywood Ubale Ibrahim rasuwa"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?