--
Ba za mu lamunci tashin farashin kayayyaki ba – Gwamna Ganduje

Ba za mu lamunci tashin farashin kayayyaki ba – Gwamna Ganduje

Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya yi ganawa ta musamman da shugabannin 'yan kasuwa a jihar da zummar daukar matakan hana tashin farashin kayayyaki.

Gwamna Ganduje ya ce ya dauki matakin ne saboda kasancewar da ma al'adace ta 'yan kasuwa idan azumi Ramadana ya zo su tashi farashin kayayyaki, "amma kasancewar ana cikin annoba ba za mu lamunci hakan ba".

A ranar Talata ne Shugaba Buhari ya saka dokar hana fita a Jihar Kano ta tsawon mako biyu bayan wadda Ganduje ya saka ta mako daya ta kare a ranar Alhamis da zummar dakile yaduwar annobar korona.




"Na tabbatar wa da 'yan kasuwar cewa zan kai korafinsu ga Aliko Dangote da Abdussamad Isiyaka Rabi'u kan farashin sikari," in ji Ganduje, a wani sakon Twitter.

"Yayin da annobar ke ci gaba da ratsawa, yana da matukar mahimmanci mu hada kai domin tsira tare."

Ya zuwa karfe 12:05 na daren 30 ga watan Afrilu, Kano ta tabbatar da mutum 139 da suka harbu da cutar korona tare da mutuwar mutum biyar.

Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya yi ganawa ta musamman da shugabannin 'yan kasuwa a jihar da zummar daukar matakan hana tashin farashin kayayyaki.

Gwamna Ganduje ya ce ya dauki matakin ne saboda kasancewar da ma al'adace ta 'yan kasuwa idan azumi Ramadana ya zo su tashi farashin kayayyaki, "amma kasancewar ana cikin annoba ba za mu lamunci hakan ba".

A ranar Talata ne Shugaba Buhari ya saka dokar hana fita a Jihar Kano ta tsawon mako biyu bayan wadda Ganduje ya saka ta mako daya ta kare a ranar Alhamis da zummar dakile yaduwar annobar korona.


"Na tabbatar wa da 'yan kasuwar cewa zan kai korafinsu ga Aliko Dangote da Abdussamad Isiyaka Rabi'u kan farashin sikari," in ji Ganduje, a wani sakon Twitter.

"Yayin da annobar ke ci gaba da ratsawa, yana da matukar mahimmanci mu hada kai domin tsira tare."

Ya zuwa karfe 12:05 na daren 30 ga watan Afrilu, Kano ta tabbatar da mutum 139 da suka harbu da cutar korona tare da mutuwar mutum biyar.



KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com



KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/


KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: BZGLOBALSERVICE.COM.NG APP

0 Response to "Ba za mu lamunci tashin farashin kayayyaki ba – Gwamna Ganduje"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?