--
Masu dauke da cutar korona sun tsere a Borno

Masu dauke da cutar korona sun tsere a Borno

Gwamnatin Borno ta ce tana neman wasu mutum biyu mace da namiji da suka tsere bayan gwaji ya tabbatar da suna dauke da cutar korona.

Sanarwar da Isa Gusau, kakakin gwamnatin jihar ya fitar ta ce namijin mai shekara 24, tun da hukumomin lafiya suka kira shi, ya kashe wayarsa, tare da kashe ta mahaifiyarsa da ake tuntubarsa.

Matar da aka bayyana shekarunta 42 ita ma ta gudu, a cewar sanarwar.

Kwamishinan lafiya na jihar Dr Kwayabura ya yi kira ga duk wanda gwaji ya tabbatar da yana dauke da cutar kada ya dauka mutuwa zai yi domin mutane da yawa sun warke daga cutar, ya gabatar da kansa a killace shi domin kada ya baza cutar ga jama'a.


KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/



KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: BZGLOBALSERVICE.COM.NG APP

0 Response to "Masu dauke da cutar korona sun tsere a Borno"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?