--
Karin mutum hudu sun kamu da coronavirus a Najeriya

Karin mutum hudu sun kamu da coronavirus a Najeriya

Hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa a Najeriy, NCDC, ta ce an samu karin mutum hudu da suka kamu da coronavirus a kasar.

A sakon da ta wallafa a Twitter ranar Talata, NCDC ta ce uku daga cikin mutanen daga Osun suke yayin da daya yake daga Ogun.

Ya zuwa yanzu ana da jumullar mutum 135 da suka kamu da cutar a Najeriya.


Awani Labarin Kuma::  Coronavirus ta yi illar da bata taba yi ba cikin kwana daya a Spain

An samu karin mutum 849 da suka mutu sakamakon coronavirus a Spain, inda ya kasance ma fi yawa da aka samu cikin kwana daya a kasar tun bullar cutar.

Ma'aikatar lafiyar kasar ta ce yanzu mutanen da suka mutu sun kai 8,189 jumulla.


Spain ce kasar da cutar ta fi yi wa illa a Turai bayan Italiya.


LATSA NAN👇👇👇 DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI TA WHATSAPP  https://chat.whatsapp.com/BztTOlXx6c183yYthtZq1Y



KU BIYOMU TA FACEBOOK FAGE DINMU KUYI LIKE DOMIN SAMUN LABARI 




b

0 Response to "Karin mutum hudu sun kamu da coronavirus a Najeriya"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?