--
Tallafin Covid-19: An gane mahaifina ba shine matsalar Najeriya ba - Zahra Buhari

Tallafin Covid-19: An gane mahaifina ba shine matsalar Najeriya ba - Zahra Buhari

 


A 'yan kwanakin da suka gabata ne 'yan Najeriya suka gano ma'adanar kayan tallafin COVID-19, kuma suka shiga suka kwashe kayan abincin tas 


Hakan ya kawo cece-kuce a kafafen sada zumuntar zamani, wanda har wata mai shirya fina-finai, Mansurah Isah ta yi wata wallafa a Instagram - Tace ga dukkan alamu, shugaba Buhari ba matsalar Najeriya bane, tunda ya bayar da kayan abinci, rabawa ne ba a yi ba,


 Zarah Buhari ta kara wallafa wannan wallafar ta Mansurah Kwanaki kadan da suka gabata, 'yan Najeriya sun gano ma'adanar da aka killace kayan abincin tallafin COVID-19 wanda CACOVID suka bayar, kuma sun fada gidajen sun kwashesu tas. 



Kayan tallafin sun hada da kayan abinci iri-iri wadanda ya kamata a rabawa talakawan Najeriya. 'Yan Najeriya da dama sun yi ta caccakar gwamnatin jihohi a kan rashin raba kayan abinci da ya kamata su yi lokacin da aka shiga tsanani. 


Wata mai shirya fina-finai, Mansurah Isah, ta wallafa a shafinta na Instagram, inda ta nuna yadda aka gano kayan tallafin, wanda hakan ke nuna ba shugaban kasa ne matsalar Najeriya ba. 


Zarah Buhari-Indimi, wacce diya ce ga shugaban kasa Muhammadu Buhari, ta kara wallafa wallafar Mansurah a shafinta na Instagram, da alamu ta yadda da abinda Mansurah Isah ta wallafa. 


Source: Legit

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A WHATSAPP:

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A TELEGRAM:


KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app75765

0 Response to "Tallafin Covid-19: An gane mahaifina ba shine matsalar Najeriya ba - Zahra Buhari "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?