--
Sai da na sake kashe wata mata bayan tserewar da na yi daga hannun ‘yan sanda – Kwararren makashi Shodipe

Sai da na sake kashe wata mata bayan tserewar da na yi daga hannun ‘yan sanda – Kwararren makashi Shodipe

Sunday Shodipe, madugun mai kashe mutane a Ibadan ya bayyana cewa ya sake kashe wata mata bayan da tsere daga ofishin yan sandan Mokola inda aka tsare shi.

Shodipe ya bayyana cewa ya gudu daga ofishin yan sanda domin aiwatar da wasu tsafe-tsafe don ra’ayin wani Idris Ajani, matsafi mai shekaru 50 wanda aka kama tare da shi.

Ya fadi hakan ne a ranar Laraba, 26 ga watan Agusta, yayinda kwamishinan yan sandan jihar Oyo, Nwachukwu Enwonwu, ya gurfanar da shi.

Wanda ake zargin ya ce matsafin ya fada masa cewa da an samu matsala sosai da bai samu ya tsere don ci gaba da kashe-kashen ba, shafin Linda Ikeji ya ruwaito.

Shodipe ya ce: “Baba (matsafin) ya sha fada ma jami’in dan sanda Funsho cewa ya bude kofa domin ya barmu mu yi wanka amma jami’in bai kula mu ba.

“Daga bisani sai Baba ya fada ma jami’in cewa yana bukatar shan barasa a matsayinsa na matsafi domin hana bakaken aljanu shanye masa jini amma jami’in ya ki kula shi.

“Baba na ta ganin laifina na fadawa ‘yan sanda da jama’a ccewa shine ya tura ni kisa sannan cewa da an sallame ni idan da na ki fadin gaskiya.

“Baba ya kuma fada mani cewa wani mummunan abu na iya faruwa da shi idan ya dade tsare a hannun yan sanda saboda wasu tsafe-tsafe da bai samu ya yi ba tun bayan da aka kama shi.

“Don haka, da dan sandan ya barni na fita wanka da yamma da misalin karfe 7:00 na yamma, sai na yi amfani da wannan damar na gudu sannan na je Akinyele na kashe wata mata.

“Baba ya tura ni waje sannan ya sani yin kisa ta hanyar ambatan sunansa, Idris Adedokun Yunusa Ajani, a cikin surkulle. Don haka sai na kashe matar domin tabbatar da tsiratar da rayuwan Baba.”

Kamar yadda kwamishinan yan sandan jihar ya tabbatar, za a mika wanda ake zargin zuwa gidan gyara halayya, wanda dama an aiye shi a ofishin yan sanda ne saboda cunkoson kurkukun jihar.


SOURCE: LEGIT.NG

DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:
https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

SAYI  KWAKWKWARAR  DATAR MTN  MAI KYAU DA INGANCI ANAN DOMIN SIYA YANZU LATSA NAN↓↓↓
https://paystack.com/pay/mz-st-fdub

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 
https://www.bzglobalservice.com.ng/

KU BIYOMU A SHAFUKAN

@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/

@TWITTER: https://twitter.com/bzglobalsevice

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Sai da na sake kashe wata mata bayan tserewar da na yi daga hannun ‘yan sanda – Kwararren makashi Shodipe "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?