--
Lauyoyin Najeriya sun yi wa El-Rufai tutsu

Lauyoyin Najeriya sun yi wa El-Rufai tutsu

Ƙungiyar Lauyoyin Najeriya ta janye gayyatar da ta yi wa Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai, biyo bayan zanga-zangar da wasu lauyoyi suka yi kan gayyatar.


A wani saƙo da Ƙungiyar Lauyoyin ta wallafa a shafinta na Twitter, ta ce ta yanke shawarar janye goron gayyatar da tura wa gwamnan kuma tuni ta shaida wa gwamnan matakin da ta ɗauka.


Tun da farko dai wani lauya ne mai suna Usani Odum ya ƙaddamar da takardar koke ta intanet inda ya nemi ƙungiyar ta janye gayyatar da ta yi wa gwamnan.


A ranar Alhamis dai sama da mutum dubu uku ne suka aika da koken su a shafin Change.org.


Masu koken akasari na zargin gwamnan da gazawa wurin shawo kan rikicin Kudancin Kaduna da kuma take haƙƙn bil adama.



 SOURCE: BBCHAUSA

DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:
https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO

SAYI  KWAKWKWARAR  DATAR MTN  MAI KYAU DA INGANCI ANAN DOMIN SIYA YANZU LATSA NAN↓↓↓
https://paystack.com/pay/mz-st-fdub

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 
https://www.bzglobalservice.com.ng/

KU BIYOMU A SHAFUKAN

@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/

@TWITTER: https://twitter.com/bzglobalsevice

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Lauyoyin Najeriya sun yi wa El-Rufai tutsu"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?